Acts 21:28 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
suna ihu suna cewa “Mutanen Isra’ila ku taimake mu! Ga mutumin da yake koya wa dukan mutane ko’ina cewa su ƙi mutanenmu da dokarmu da kuma wannan wuri. Ban da haka ma, ya kawo Hellenawa a cikin filin haikali ya ƙazantar da wurin nan mai tsarki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُنَ إِيهُ سُنَ ثٜىٰوَ «كُو یَنْعُوَ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا، كُتَيْمَكَ! غَا مُتُمِنَّنْ دَ يَكٜىٰبِے كُواْعِنَ يَنَ ذَاغِنْ مُتَنٜىٰنْمُ دَ كُواْيَرْوَرْمُ دَ كُمَ وَنَّنْ هَيْكَلِنْمُ؞ حَرْ مَا يَكَٰوُاْ وَطَنْسُ هٜىٰلٜىٰنَاوَا عَثِكِنْ هَيْكَلِ يَڧَظَنْتَرْ دَ وُرِنَّنْ مَيْ ڟَرْكِے؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
suna ihu suna cewa, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, ku taimaka! Ga mutumin da yake bi ko'ina yana koya wa mutane su raina jama'armu da Shari'a, da kuma wannan wuri. Banda haka kuma har ma ya kawo al'ummai a cikin Haikalin, ya ƙazantar da wurin nan tsattsarka.”