Acts 25:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Na gaya musu cewa ba al’adar Romawa ba ce a hukunta mutum kafin ya fuskanci masu ƙararsa ya kuma sami damar kāre kansa game da ƙararsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا نَا غَيَ مُسُ ثٜىٰوَ مُو رُواْمَاوَا بَمُسَابَايِ وَمَيْ لَيْڢِے شَرِيعَبَ، سَيْ أَنْكَٰوُاْ شِ أَغَبَنْ مَاسُ ڧَارَرْسَ ڢُسْكَ دَ ڢُسْكَ، سَيْ أَنْكُمَ بَاشِ ظَرَڢِ دُواْمِنْ يَكَارٜىٰ كَنْسَ غَمٜىٰدَ ڧَارَرْ دَ عَكَيِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ni kuwa na amsa musu na ce, ba al'adar Romawa ba ce a yi wa wani hukunci, don faranta wa wani rai, ba tare da masu ƙarar, da wanda aka kai ƙara, sun kwanta a gaban shari'a ba, ya kuma sami damar kawo hanzarinsa game da ƙarar da aka tāsar.