Acts 4:24 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُو كُوَ دَ جِنْ حَكَ، سَيْ سُكَ طَغَ مُرْيَرْسُ غَ اللَّهْ دَ نُڢِ طَيَ سُكَثٜىٰ، « عُبَنْ‌غِجِ مَيْ إِيكُواْ دُكَ ، كَيْنٜىٰ كَا حَلِثِّ سَمَ دَ ڧَسَا دَ تٜىٰكُ دَ كُمَ دُكَنْ أَبُبُوَنْ دَسُكٜىٰ ثِكِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Su kuwa da jin haka, sai suka ɗaga muryarsu ga Allah da nufi ɗaya, suka ce, “Ya Mamallaki, Mahaliccin sama, da ƙasa, da teku, da kuma dukkan abin da yake a cikinsu,