Acts 6:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai hamayya ta taso daga ’yan ƙungiyar Majami’a na ’Yantattu (kamar yadda ake kiransu), Yahudawan Sairin da Alekzandariya da kuma lardunan Silisiya da Asiya. Mutanen nan suka fara muhawwara da Istifanus,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ وَطَنْسُ نَمَجَمِعَرْ دَ عَكٜىٰثٜىٰ دَ عِتَ مَجَمِعَرْ یَنْتَتُّ، سُكَ تَيَرْوَ إِسْتِڢَنُسْ دَ غَرْدَمَ؞ وَطَنَّنْ كُوَ يَهُودَاوَا نٜىٰ دَغَ سَيِرِنْ دَ إِسْكَنْدَارِيَا دَ كُمَ دَغَ ڧَسَرْ كِلِكِيَ دَ تَ أَسِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan waɗansu na majami'ar da ake kira majami'ar Libartinawa, wato Kuraniyawa da Iskandariyawa, da kuma waɗansu daga ƙasar Kilikiya da ta Asiya, suka tasar wa Istifanas da muhawwara.