Acts 7:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَكُمَ ڢِتَرْ دَشِ دَغَ دُكَنْ وَهَلَرْسَ؞ اللَّهْ كُمَ يَسَا يَذَمَ مَيْ حِكِمَ، مَيْ ڢَضٍ جِنِ أَغَبَنْ سَرْكِے ڢِرْعَوْنَ نَ مَصَرْ؞ ڢِرْعَوْنَ كُوَ يَمَيْدَ يُوسُڢَ ڠُومْنَ نَڧَسَرْ مَصَرْ دَ كُمَ شُوغَبَنْ دُكَنْ جَمَعَرْ غِدَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ya kuma tsamo shi daga dukan wahala tasa, ya ba shi farin jini da hikima a gun Fir'auna, Sarkin Masar, shi kuwa ya naɗa shi mai mulkin Masar, ya kuma danƙa masa jama'ar gidansa duka.