Acts 8:27 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka ya kama hanya, a kan hanyarsa kuwa sai ya sadu da wani mutumin Itiyofiya, wanda yake bābā, hafsa mai muhimmanci wanda yake lura da dukan ma’ajin Kandas (wanda yake nufin “sarauniyar mutanen Itiyofiya”). Mutumin nan ya tafi Urushalima ne domin yin sujada,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَتَاشِ يَتَڢِے؞ سَيْغَا وَنِ مُتُمِنْ إِتِيُواْڢِيَ وَنْدَ شِے بَابَا نٜىٰ، وَتُواْ أَنْدَنْدَڧٜىٰشِ، مَيْ بَبَّنْ مَڟَيِ أَمُلْكٍ كَنْدِسْ، سَرَوْنِيَرْ إِتِيُواْڢِيَ؞ شِينٜىٰ كُمَ مَعَجِنْ سَرَوْنِيَرْ؞ يَذُواْ عُرُوشَلِيمَ نٜىٰ دُواْمِنْ يَيِ سُجَّدَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya tashi ya tafi. Ga wani mutumin Habasha, wani bābā, mai babban matsayi a mulkin Kandakatu, sarauniyar Habasha, shi ne kuwa ma'ajinta, ya zo Urushalima ne yin sujada,