Acts 9:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A Damaskus kuwa akwai wani almajiri mai suna Ananiyas. Ubangiji ya kira shi a cikin wahayi ya ce, “Ananiyas!” Ananiyas ya amsa, “Ga ni, ya Ubangiji.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُواْ، أَݣَويْ وَنِ مَيْبِے أَ دِمَشْڧُ، مَيْ سُونَ هَنَنِيَ؞ عُبَنْ‌غِجِ يَيِ مَسَ مَغَنَ ثِكِنْ رُعُيَ يَثٜىٰ «هَنَنِيَ!» شِے كُوَ يَأَمْسَ «غَا نِے، يَا عُبَنْ‌غِجِ ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
To, akwai wani mai bi a Dimashƙu, mai suna Hananiya. Ubangiji ya yi masa magana cikin wahayi ya ce, “Hananiya.” Shi kuwa ya ce, “Na'am, ya Ubangiji.”