Acts 9:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Ananiyas ya tafi gidan ya kuma shiga ciki. Da ya sa hannuwansa a kan Shawulu, sai ya ce, “Ɗan’uwana Shawulu, Ubangiji, Yesu, wanda ya bayyana gare ka a kan hanya yayinda kake zuwa nan, ya aiko ni domin ka sāke gani a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ هَنَنِيَ يَتَڢِے يَشِغَ غِدَنْ؞ يَسَ حَنُّوَنْسَ عَكَنْ شَوُلُ، يَثٜىٰ «طَنْعُوَنَ شَوُلُ، عُبَنْغِجِ نٜىٰ يَعَيْكُواْ نِے، وَتُواْ عِيسَىٰ وَنْدَ يَبَيَّنَ أَغَرٜىٰكَ عَكَنْ حَنْيَرْدَ كَبِيُواْ؞ يَعَيْكٜىٰنِ دُواْمِنْ كَسَاكٜىٰ عِيَ غَنِ، عَكُمَ ثِكَكَ دَ رُوحُ مَيْ ڟَرْكِے ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Da ya ɗora masa hannu, ya ce, “Ya ɗan'uwana Shawulu, Ubangiji ne ya aiko ni, wato Yesu, wanda ya bayyana a gare ka a kan hanyar da ka biyo, domin ka sāke gani, a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”