Acts 9:27 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Barnabas ya ɗauke shi ya kawo shi wurin manzanni. Ya gaya musu yadda Shawulu a kan hanyarsa ya ga Ubangiji kuma cewa Ubangiji ya yi magana da shi, da yadda a Damaskus ya yi wa’azi ba tsoro a cikin sunan Yesu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا بَرْنَبَ يَطَوْكٜىٰشِ يَكَيْ شِ وُرِنْ مَنْذَنِّے؞ يَڢَطَا مُسُ يَدَّ شَوُلُ يَغَ عُبَنْ‌غِجِ أَ حَنْيَ دَ يَدَّ عُبَنْ‌غِجِ يَيِ مَسَ مَغَنَ دَ كُمَ يَدَّ شَوُلُ يَيِ وَعَظِ دَ سُونَنْ عِيسَىٰ أَ دِمَشْڧُ، بَ ڟُواْرُواْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Barnaba ya kama hannunsa ya kai shi wurin manzannin, ya gaya musu yadda Shawulu ya ga Ubangiji a hanya, da yadda Ubangiji ya yi masa magana, da kuma yadda ya yi wa'azi gabagaɗi da sunan Yesu a Dimashƙu.