Amos 1:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، «مُتَنٜىٰنْ عٜىٰدُوامْ سُنْيِ ذُنُوبِنْ غَنْغَنْثِ، سُكَڧَارَ ذُنُوبِ عَكَنْ ذُنُوبِ؞ بَذَنْ دَيْنَ حُكُنْتَسُبَ، دُواْمِنْ سُنْبِے طَنْعُوَنْسُ دَ تَكُواْبِے، سُنْ بِے إِسْرَٰٓءِيلَ بَابُ تَوْسَيِ؞ ڢُشِنْ مُتَنٜىٰنْ عٜىٰدُوامْ يَيِ تَهَوْكَ، سُنْ رِڧٜىٰ ڢُشِنْسُ كَمْكَمْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce, “Mutanen Edom sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun farauci 'yan'uwansu, Isra'ilawa, Suka ƙi su nuna musu jinƙai. Ba su yarda su huce daga fushinsu ba.