Amos 1:5 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَنْ كَكَّرْيَ ڧَرَڢَنْ ڧُواْڢَرْ دِمَشْڧُ، إِنْكَوَرْدَ مَذَوْنَنْ ݣُورِنْ أَوٜىٰنْ؞ ذَنْ كَشٜىٰ سَرْكِنْ بٜىٰتٜىٰدٜىٰنْ، مُتَنٜىٰنْ سُورِيَ كُوَ ذَاسُ تَڢِے بَوْتَا عَڧَسَرْ كِرْ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ ، نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zan ragargaje ƙyamaren ƙofofin birnin Dimashƙu, In kawar da masu sarautar Bet-eden da na kwarin Awen. Za a kwashe mutanen Suriya ganima zuwa ƙasar Kir.”