Amos 8:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun ’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ «عَمُواسْ، مٜىٰ كَغَنِ؟» سَيْ نَثٜىٰ «نَغَ ݣُونْدُوانْ یَیَنْ إِتَاثٜىٰنْ دَ سُكَ نُونَ؞» سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ، «كَمَرْ يَدَّ یَیَنْ إِتَاثٜىٰنَّنْ سُنْ كَيْ يَدَّ ذَاعَ ثِ، حَكَ ذُنُبَنْ مُتَنٜىٰنَ سُنْ كَيْ يَدَّ ذَاعَ حُكُنْتَسُ؞ ڧَرْشٜىٰ يَذُواْ وَمُتَنٜىٰنَ إِسْرَٰٓءِيلَ، بَذَنْ ڧَارَ ڨَلٜىٰ ذُنُبَنْسُبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Ubangiji ya ce, “Amos, me ka gani?” Na ce, “Kwandon ɓaure na ci.” Ubangiji kuma ya ce mini, “Ƙarshen jama'ata Isra'ila ya zo. Ba zan sāke nufina a kan yi musu hukunci ba.