Colossians 2:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya yanke dangantaka da Kiristi wanda yake kai, wanda ta gare shi ne dukan jiki yake a haɗe, yake tsaye ta wurin taimakon gaɓoɓi da jijiyoyi, yana kuma girma kamar yadda Allah yake sa yă yi girma.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَيْ، إِرِنْ وَنَّنْ مُتُمْ بَيْ مَنّٜىٰوَ أَلْمَسِيحُ بَ، وَنْدَ شِينٜىٰ كَيْ نَجِكِے؞ غَمَا شِے يَنَ رِڧٜىٰ دَ دُكَنْ جَمَعَرْ مَاسُبِے، وَتُواْ جِكِنْسَ، وَنْدَ يَكٜىٰ أَ حَطٜىٰ تَوُرِنْ غَٻُواْٻِ دَ جِجِيُواْيِ، يَنَ كُمَيِنْ غِرْمَ دَ غِرْمَنْ دَ اللَّهْ يَكٜىٰ سَاوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
bai kuwa manne wa kan ba, wanda ta gare shi ne dukkan jiki yake amfana, yake kuma a haɗe, ta wurin gaɓoɓi da jijiyoyi, yake kuma girma da girman da Allah yake sawa.