Daniel 1:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عُبَنْغِجِ كُوَ يَبَا سَرْكِے نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ نَ بَابِيلَ نَصَرَا عَكَنْ سَرْكِے يٜىٰهُواْيَكِمْ نَ يَهُودَ؞ سَرْكِے نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ كُوَ يَݣُوشٜىٰ وَطَنْسُ كَايَ دَغَ ثِكِنْ غِدَنْ اللَّهْ أَ عُرُوشَلِيمَ؞ كَايَنَّنْ يَكَٰوُاْسُ أَغِدَنْ اللَّهْنْسَ عَڧَسَرْ شِنَرْ، يَأَجِيٜىٰسُ أَطَاكِنْ أَجِيَ نَ اللَّهْ نْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji kuwa ya ba Nebukadnezzar nasara a kan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, sai ya kwashe waɗansu kayayyakin Haikalin Allah, ya kawo su ƙasar Shinar a gidan gunkinsu, ya ajiye kayayyakin a baitulmalin gunkinsa.