Daniel 1:4 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَطَنَّنْ سَمَارِ ذَاسُ كَسَنْثٜىٰ مَاسُ ݣَنْ غَنِ، مَرَرْ تَبُواْ، مَاسُثِكٜىٰ دَ ڢَهِمْتَ دَ كُواْوَنٜىٰ ڢَنِّنْ حِكِمَ دَ سَنِ، مَاسُ عِيَيِنْ حِدِمَ أَغِدَنْ سَرْكِے؞ ذَاعَكُواْيَ مُسُ يَرٜىٰنْ مُتَنٜىٰنْ بَابِيلَ دَ أَبُبُوَنْ دَسُكٜىٰ ثِكِنْ لِتَّتَّڢَنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
su kasance samari ne kyawawa, waɗanda ba su da wata naƙasa, masu fasaha cikin kowane abu, masu fahimta, da masu saurin ganewa, waɗanda suke da halin iya hidima a fādar sarki. Nebukadnezzar ya umarci Ashfenaz ya koya musu littattafan Kaldiyawa da harshen Kaldiyawa.