Daniel 2:28 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا إِنَ سُواْ إِنْ تَبَّتَرْوَ سَرْكِے ثٜىٰوَ أَݣَويْ اللَّهْ أَ سَمَ وَنْدَ شِينٜىٰ مَيْ بَيَّنَ أَسِرَيْ؞ وَنَّنْ اللَّهْ شِينٜىٰ يَسَنَرْ وَسَرْكِے أَبِنْدَ ذَيْ ڢَرُ نَنْ غَبَ؞ رَنْكَيَدَطٜىٰ! تُواْ، يَنْذُ ذَنْ ڢَطَا مَكَ مَڢَرْكِ دَ رُعُيَرْدَ كَغَنِ، سَعَدَّ كَكٜىٰ ݣُونْثٜىٰ عَكَنْ غَدُوانْكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma akwai Allah a Sama mai bayyana asirai, shi ne ya sanar wa sarki Nebukadnezzar da abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayinka waɗanda suka zo cikin tunaninka, sa'ad da kake kwance bisa gadonka ke nan.