Daniel 3:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Nebukadnezzar ya matsa kusa da ƙofar tanderun wutar ya yi kira da ƙarfi, “Shedrak, Meshak da Abednego, bayin Allah Mafi Ɗaukaka ku fito! Ku zo nan!” Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka fita daga cikin wutar,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ ڢَا يَمَڟُواْ كُسَدَ ڧُواْڢَرْ غِدَنْ وُتَا مَيْ ذَاڢِ يَثٜىٰ «شَدْرَكْ! مٜىٰشَكْ! أَبٜىٰدْنٜىٰغُواْ! بَايِنْ اللَّهْ مَڢِے طَوْكَكَ ، كُڢِتُواْ! كُذُواْ نَنْ!» سَيْ شَدْرَكْ دَ مٜىٰشَكْ دَ أَبٜىٰدْنٜىٰغُواْ سُكَ ڢِتَ دَغَ ثِكِنْ وُتَرْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Nebukadnezzar fa ya matso kusa da ƙofar tanderun gagarumar wuta, ya ce, “Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, bayin Allah Maɗaukaki, ku fito, ku zo nan!” Sai Shadrak, da Meshak, da Abed-nego suka fita daga cikin wutar.