Daniel 3:28 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allahn Shadrak, Meshak da Abednego wanda ya aiko da mala’ikansa ya ceci bayinsa da suka dogara matuƙa a gare shi, suka ki bin umarnin sarki kuma su na a shirye domin su ba da ransu da suka ƙi bauta ko su yi sujada ga wani allah sai dai Allahnsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ يَثٜىٰ «يَبُواْ يَتَبَّتَا غَ اللَّهْ نَ شَدْرَكْ دَ مٜىٰشَكْ دَ أَبٜىٰدْنٜىٰغُواْ، وَنْدَ يَعَيْكُواْ دَ مَلاَىِٕكَنْسَ يَكُٻُتَرْدَ بَايِنْسَ مَاسُ دُواْغَضَ غَرٜىٰشِ؞ سُنْڧِے بِنْ عُمَرْنِنْ سَرْكِے، سُكَ ڠُومَّثٜىٰ عَڧُواْنٜىٰسُ مَيْمَكُوانْ سُبَوْتَاوَ غُنْكِ كُواْ سُيِ وَوَنِ سُجَّدَ، إِنْ بَ دَيْ اللَّهْ نْسُ كَطَيْبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allah na Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, wanda ya aiko da mala'ikansa, ya ceci bayinsa masu dogara gare shi, waɗanda kuma ba su yarda su bi umarnin sarki ba, amma suka gwammace a ƙone su maimakon su bauta wa gunki, ko su yi masa sujada, sai dai ga Allahnsu kaɗai.