Daniel 4:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ دَانِيٜىٰلْ وَنْدَ عَكَ كُمَ سَنْ شِ دَ سُونَ بٜىٰلْتٜىٰشَظَّرْ، يَڟَيَ شِضُ نَطَنْ لُواْكَثِ أَ ضِكِثِے سَبُواْدَ تُنَانِنْسَ يَبَا شِ ڟُواْرُواْ؞ سَيْ سَرْكِے يَثٜىٰ مَسَ «بٜىٰلْتٜىٰشَظَّرْ، كَدَ كَبَرْ مَڢَرْكِنْ كُواْ مَعَنَرْسَ يَبَاكَ ڟُواْرُواْ؞» سَيْ بٜىٰلْتٜىٰشَظَّرْ يَأَمْسَ يَثٜىٰ «يَا مَيْغِرْمَ، بَرِ اللَّهْ يَسَا مَڢَرْكِنَّنْ دَ مَعَنَرْسَ سُذَمَ عَكَنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْكَ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Daniyel kuwa wanda aka laƙaba wa suna Belteshazzar, ya tsaya zugum da ɗan daɗewa, tunaninsa ya ba shi tsoro. Sarki ya ce, “Belteshazzar, kada ka bar mafarkin ko ma'anarsa ya ba ka tsoro.” Sai Belteshazzar ya amsa, ya ce, “Ya shugabana, Allah ya sa mafarkin nan, da ma'anarsa, su zama a kan maƙiyanka.