Daniel 5:23 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ مَيْمَكُوانْ حَكَ، سَيْ كَنُونَوَ عُبَنْغِجِنْ سَمَ غِرْمَنْ كَيْ، حَرْ كَسَا عَكَ كَٰوُاْ مَكَ ݣُوڢُنَنْ غِدَنْسَ؞ كَيْ دَ مَنْيَنْ مُتَنٜىٰنْكَ دَ مَاتَنْكَ دَ مَاتَانْدَ كَأَجِيٜىٰ دُكَنْكُ كُكَ شَا دَغَ ثِكِنْسُ؞ كُكَ يَبِے غُمَكَنْ ظِينَارِيَ دَ نَأَظُرْڢَا دَ نَتَغُلَّ دَ نَبَڧِنْ ڧَرْڢٜىٰ دَ نَ إِتَاثٜىٰ دَ نَدُوڟٜىٰ وَطَنْدَ بَاسَجِ، كُواْ سُغَنِ، بَلّٜىٰ عَثٜىٰ سُغَانٜىٰ كُواْمٜىٰ؞ عَمَّا اللَّهْ وَنْدَ رَنْكَ دَ دُكَنْ هَنْيُواْيِنْكَ سُنَ أَ حَنُّنْسَ، شِينٜىٰ كَاڧِ غِرْمَمَاوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Maimakon haka, sai ka nuna wa Ubangiji girmankai, har ka sa aka kawo maka, kai da fādawanka, da matanka, da ƙwaraƙwaranka, tasoshin Haikalin Ubangiji, kuka sha ruwan inabi a cikinsu. Kuka yabi gumakan zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba su ji, ba su gani, ba su da ganewar kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.