Daniel 5:3 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عَكَ كَٰوُاْ ݣُوڢُنَ نَظِينَارِيَ دَ نَأَظُرْڢَا وَطَنْدَ عَكَ ݣُوشٜىٰ دَغَ هَيْكَلِ، وَتُواْ غِدَنْ اللَّهْ أَ عُرُوشَلِيمَ؞ سَيْ سَرْكِے دَ مَنْيَنْ مُتَنٜىٰنْسَ دَ مَاتَنْسَ دَ مَتَنْ دَ يَأَجِيٜىٰ سُكَشَا دَغَ ثِكِنْ ݣُوڢُنَنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai suka kawo tasoshin zinariya da na azurfa waɗanda aka kwaso daga cikin Haikali, wato Haikalin Allah a Urushalima. Sai sarki da manyan mutanensa, da matansa, da ƙwaraƙwaransa, suka yi ta sha da su.