Daniel 5:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے يَيِ كِرَا دَ بَبَّرْ مُرْيَ دُواْمِنْ عَكَٰوُاْ مَسَ مَاسُ دُوبَادَ ڠُونَيٜىٰنْ ڟَاڢِ دَ مَاسُ يِنْ دُوبَادَ تَوْرَرِ؞ سَيْ سَرْكِے يَيِ مَغَنَ غَمٜىٰدَ مَاسُ حِكِمَرْ نَنْ يَثٜىٰ «دُكْ وَنْدَ يَ عِيَ كَرَنْتَ وَنَّنْ رُبُوتُو، يَكُوَ ڢَطَا مِنِ مَعَنَرْسَ، تُواْ، ذَاعَ سَا مَسَ رِغَرْ مُلْكِ تَجَرْ غَرُورَا، أَسَا مَسَ سَرْڧَرْ ظِينَارِيَ أَوُيَنْسَ، ذَاعَ كُمَ بَاشِ مَڟَيِ نَعُكُ عَثِكِنْ مَاسُ مُلْكٍ ڧَسَرْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai sarki ya yi kira da babbar murya, cewa a kawo masu dabo, da bokaye, da masu duba. Sai sarki ya ce wa masu hikima na Babila, “Dukan wanda ya karanta wannan rubutu, ya faɗa mini ma'anarsa, to, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”