Daniel 7:27 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُلْكِ دَ إِيكُوانْ مُلْكِ دَ غِرْمَنْ دُكَنْ مُلْكُواْكِ عَڧَرْڧَشِنْ سَمَ، ذَاعَ بَادَسُو غَ ڟَرْكَكَا، غَ مُتَنٜىٰنْ مَڢِے طَوْكَكَ ؞ مُلْكِنْسَ ذَيْ كَسَنْثٜىٰ نَهَرْ أَبَدَا نٜىٰ؞ دُكَنْ سَرَاكُنَنْ دُونِيَا ذَاسُ بَوْتَا مَسَ، سُكُمَيِ مَسَ بِيَيَّ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan za a ba da sarauta da girman dukan mulkokin duniya ga tsarkaka na Maɗaukaki. Mulkinsa madawwamin mulki ne. Dukan sarakunan duniya za su bauta masa, su kuma yi masa biyayya.’