Daniel 8:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مَلاَىِٕكَ جِبْرِيلُ يَمَڟُواْ كُسَدَ عِنْدَ نَكٜىٰ ڟَيٜىٰ؞ دَ يَذُواْ، سَيْ نَڢِرْغِتَ، نَڢَاطِ دَ ڢُسْكَتَ حَرْ ڧَسَا؞ عَمَّا يَثٜىٰ مِنِ «يَا كَيْ طَنْ أَدَمْ، سَيْ كَغَانٜىٰ ثٜىٰوَ وَنَّنْ رُعُيَرْ تَشَاڢِ ݣُونَكِنْ ڧَرْشٜىٰنٜىٰ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Don haka sai ya zo kusa da inda nake tsaye. Da ya zo sai na firgita, na faɗi rubda ciki. Amma ya ce mini, “Ɗan mutum, wannan wahayi yana a kan lokaci na ƙarshe ne.”