Daniel 9:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya Ubangiji, ta wurin kiyaye dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hukuncinka da ka yi a kan Urushalima, birninka, tudunka mai tsarki. Zunubinmu da laifofin iyayenmu sun mai da Urushalima da kuma mutanenka abin ba’a ga dukan waɗanda suke kewaye da mu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا عُبَنْ‌غِجِ ، بِسَغَ دُكَنْ أَيُّكَنْكَ نَأَدَلْثِے، إِنَ ضُواْڧُوانْكَ، بَرِ كَجَنْيٜىٰ ڢُشِنْكَ مَيْ ذَاڢِ وَنْدَ كَيِ دَ بِرْنِنْكَ عُرُوشَلِيمَ، تُدُنْكَ مَيْ ڟَرْكِے؞ غَمَا سَبُواْدَ ذُنُبَنْمُ دَ لَيْڢُواْڢِنْ كَاكَنِّنْمُ، عُرُوشَلِيمَ دَ جَمَعَرْكَ سُنْ ذَمَ أَبِنْ بَعَ غَ دُكَنْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَمُو؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya Ubangiji, saboda dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hasalarka da ka yi da birninka Urushalima, tsattsarkan tudunka. Gama saboda zunubanmu da muguntar kakanninmu, Urushalima da jama'arka sun zama abin ba'a ga waɗanda suke kewaye da mu.