Daniel 9:18 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ka kasa kunne, ya Allah, ka kuma ji; ka buɗe idanunka ka kuma ga yadda birninka ya zama kango, birnin da yake ɗauke da Sunanka. Ba cewa muna roƙonka saboda mu masu adalci ba ne, amma saboda girman jinƙanka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا اللَّهْ نَا، كَسَ كُنّٜىٰنْكَ كَجِ، بُوطٜىٰ عِدَنُونْكَ كَدُوبَ يَدَّ مُو دَ بِرْنِنْ دَ عَكٜىٰ كِرَا دَ سُونَنْكَ مُكَ لَلَثٜىٰ؞ غَمَا بَمُ كَٰوُاْ ضُواْڧٜىٰ ضُواْڧٜىٰنْمُبَ سَبُواْدَ وَيْ مُنَدَ أَدَلْثِے، عَمَّا سَبُواْدَ يَوَنْ جِنْڧَنْكَنٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya Allahna, ka karkato kunnenka ka ji, ka buɗe idanunka ka ga yadda mu da birnin da ake kira da sunanka muka lalace. Ba cewa muna da wani adalci na kanmu shi ya sa muka kawo roƙe-roƙenmu ba, amma saboda yawan jinƙanka.