Deuteronomy 1:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُوسَٰى يَثِيغَبَدَ مَغَنَ ثٜىٰوَ «كُتُنَ يَدَّ مُكَتَاشِ دَغَ بَبَّنْ تُدُنْ هُواْرٜىٰبْ، كَمَرْ يَدَّ يَهْوٜىٰهْ يَعُمَرْثٜىٰمُ، مُكَبِے تَبَبَّنْ دَاجِنَّنْ مَيْ بَنْ ڟُواْرُواْ وَنْدَ كُو دَ كَنْكُ كُكَ غَنِ، يَايِنْ دَمُكٜىٰ أَ حَنْيَرْمُ ذُوَا يَنْكِنْ تُدَّيْ نَ أَمُواْرِيَاوَا؞ سَعَدَّ مُكَ إِسُواْ كَدٜىٰشْ بَرْنٜىٰيَ،
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Sai muka tashi daga Horeb, muka ratsa babban jejin nan mai bantsoro wanda kuka gani a hanyarmu zuwa ƙasar tuddai ta Amoriyawa, kamar yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu, muka zo Kadesh-barneya.