Deuteronomy 1:28 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ina za mu? ’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنَا نٜىٰ ذَامُجٜىٰ؟ یَنْ لٜىٰڧٜىٰنْ أَسِيرِ سُنْ كَرْيَ مَنَ ڠُوِوَ دَ رَهُواْتُوانْسُ؞ سُكَثٜىٰ «مُتَنٜىٰنْ ڧَسَرْ سُنْ ڢِمُ ڧَرْڢِے كُمَ مَاسُ ڟَيِ نٜىٰ ڢِيٜىٰ دَمُو؞ بِرَنٜىٰنْسُ مَنْيَ مَنْيَ نٜىٰ، كَتَنْغَرْسُ كُمَ سُنَدَ ڟَيِ ڨُورَيْ؞ حَرْ مَا مُنْ غَا ذُرِيَرْ یَیَنْ أَنَكْ أَوُرِنْ!» ›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ta ƙaƙa za mu hau? Gama 'yan'uwanmu sun narkar da zuciyarmu da cewa, mutanen sun fi mu girma, sun kuma fi mu ƙarfi. Biranensu kuma manya manya ne, da gine-gine masu tsayi ƙwarai. Har ma sun ga Anakawa a wurin.’