Deuteronomy 12:11 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato, hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakkarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na alkawarin da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă sa sunansa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً ذَاكُ كَيْ دُكَنْ أَبِنْدَ نَعُمَرْثٜىٰكُ كُكَيْ ذُوَا وُرِنْ دَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ ذَيْ ذَاٻَا دُواْمِنْ عَيِ سُجَّدَ دَ سُونَنْسَ، وَتُواْ ذَاكُ كَيْ هَدَايُنْكُ نَڧُواْنَاوَا دَ سَوْرَنْ هَدَايُنْكُ دَ زَكَّرْكُ دَ بَيٜىٰ بَيٜىٰنْكُ نَغُواْدِيَ دَ هَدَايُنْكُ مَڢِے ݣَوْ نَثِكَ ضَنْڟُوَا وَ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na wa'adi da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa ya sa sunansa.