Deuteronomy 12:18 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A maimakon haka, sai ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, da ku da ’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da kuma Lawiyawa daga biranenku, ku kuwa yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a kowane abin da kuka sa hannunku.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا وَطَنَّنْ ذَاكُثِسُ أَغَبَنْ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ أَ عِنْدَ ذَيْ ذَاٻَا، كُو دَ یَیَنْكُ مَظَا دَ مَاتَادَ بَايِنْكُ مَظَا دَ مَاتَادَ لَوِيَاوَنْ دَسُكٜىٰ ظَوْنٜىٰ أَغَرُرُوَنْكُ؞ سَيْ كُيِ مُرْنَ أَغَبَنْ يَهْوٜىٰهْ دَ دُكَنْ أَيُّكَنْ حَنُّوَنْكُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma sai ku ci su a inda Ubangiji Allahnku zai zaɓa, ku da 'ya'yanku mata da maza, da barorinku mata da maza, da Lawiyawa da suke a cikin garuruwanku. Sai ku yi murna a gaban Ubangiji Allah saboda duk abin da kuke yi.