Deuteronomy 13:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُكَنْ أَبُبُوَنْ دَ كُكَ ݣُوشٜىٰ كُتَتَّارَ أَ ڢِيلِ نَثِكِنْ غَرِنْ؞ سَيْ كُڧُواْنَ غَرِنْ دَ دُكَنْ أَبُبُوَنْ دَ كُكَ ݣُوشٜىٰ، كُمِيڧَ شِ طُنْ‌غُمْ هَدَايَ تَڧُواْنَاوَا غَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ؞ غَرِنْ كُوَ ذَيْ كَسَنْثٜىٰ كُڢَيْ حَرْ أَبَدَا، بَذَاعَ ڧَارَ غِنَاشِ بَكُمَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ku tattara dukan ganimar garin a dandali, ku ƙone garin da dukan ganimar, hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji Allahnku. Garin zai zama kufai har abada, ba za a ƙara gina shi ba.