Deuteronomy 15:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
In akwai matalauci a cikin ’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«عِدَنْ أَݣَويْ مَيْ بُڧَاتَ عَثِكِنْكُ، وَتُواْ وَنِ دَغَ ثِكِنْ یَنْعُوَنْكُ عَثِكِنْ غَرُضُوً ڧَسَرْدَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ يَكٜىٰ بَاكُ، كَدَ كُتَوْرَرَ ذُوثِيَارْكُ، كُكَاسَ سَكِ حَنُّنْ تَيْمَكُواْ غَ طَنْعُوَنْكُ مَيْ بُڧَاتَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Idan akwai wani danginku matalauci, a wani gari na cikin garuruwan ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, to, kada ku taurara zuciyarku, ku ƙi sakin hannu ga danginku matalauci.