Deuteronomy 19:5 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مِصَالِ، عِدَنْ وَنِ يَشِغَ ثِكِنْ كُرْمِ دَ وَنِ دُواْمِنْ سَارَنْ إِتَاثٜىٰ، طَيَنْ كُمَ يَنَ سَارَ، سَيْ كَنْ غَاتَرِنْ يَݣُوٻٜىٰ دَغَ ڧُواْتَرْ يَبُغِ طَيَنْ مُتُمْ حَرْ يَمُتُ، شِے وَنْدَ يَيِ كِسَنْ كَيْ طِنْ، ذَيْ عِيَ غُدُ ذُوَا طَيَ دَغَ ثِكِنْ غَرُرُوَنَّنْ، ذَيْ كُوَ ثٜىٰثِ رَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
misali, idan mutum ya tafi jeji, shi da abokinsa don su saro itace. Da ya ɗaga gatari don ya sari itace, sai ruwan gatarin ya kwaɓe daga ƙotar, ya sari abokinsa har ya mutu. Irin wannan mai kisankai zai gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen don ya tsira,