Deuteronomy 2:23 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمٜىٰ دَ أَوِّيَاوَا وَطَنْدَ سُكَ ذَوْنَ عَڧَوْيُكَنْ دَسُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَ غَاظَ، كِرِتَاوَا، وَتُواْ ڢِلِسْتِيَاوَا، سُكَذُواْ دَغَ ڟِبِرِنْ كِرِتْ سُكَ هَلَكَاسُ سُكَ ذَوْنَ أَوُرِنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Haka nan kuma ya faru da Awwiyawa mazaunan ƙauyukan da suke kewaye da Gaza, wato su Kaftorawa waɗanda suka zo daga Kaftor, suka hallakar da su, suka zauna a wurinsu.)