Deuteronomy 2:30 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«عَمَّا سَرْكِے سِهُوانْ نَ هٜىٰشْبُوانْ، بَيْ يَرْدَ مَنَ مُوُثٜىٰبَ، غَمَا يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ يَتَوْرَرَ ذُوثِيَارْسَ دَ حَنْكَلِنْسَ، دُواْمِنْ يَبَادَشِ أَ حَنُّنْكُ، كَمَرْ يَدَّ يَنْذُ يَيِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Amma Sihon, Sarkin Heshbon, ya ƙi yarda mu wuce, gama Ubangiji Allahnku ya riga ya taurare hankalinsa da zuciyarsa don ya bashe shi a hannunku, kamar yadda yake a yau.