Deuteronomy 25:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
In ’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«سَعَدَّ یَنْعُوَ مَظَا سُنَ ظَوْنٜىٰ أَوُرِے طَيَ تَرٜىٰ، سَيْ طَيَنْسُ يَمُتُ بَيْ حَيْڢُ بَ، مَاتَرْ وَنْدَ يَمُتُ طِنْ بَذَاتَ ڢِتَ تَ عَوْرِ وَنِ بَڧُواْ وَنْدَ بَدَغَ ثِكِنْ یَنْعُوَنْ مِجِنْبَ؞ سَيْ طَنْعُوَنْ مِجِنْتَ يَذُواْ وُرِنْتَ، يَ عَوْرٜىٰتَ، يَثِكَ حَكِّنْ طَنْعُوَنْ مِجِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Idan 'yan'uwa suna zaune wuri ɗaya tare, in ɗayansu ya rasu bai haihu ba, to, kada matar marigayin ta auri wani baƙo wanda yake ba a cikin dangin mijin ba. Sai ɗan'uwan mijinta ya zo wurinta, ya aure ta, ya yi mata abin da ya kamaci ɗan'uwan miji ya yi.