Deuteronomy 27:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
« ‹لَعَنَنّٜىٰ نٜىٰ مُتُمِنْدَ يَسَسَّڧَ غُنْكِ كُواْ يَيِ ظُبِنْ غُنْكِنْ أَلُّواْلِ نَڧَرْڢٜىٰ، عَيْكِنْ ڠُونِ، سَيْ يَاكَڢَشِ أَوَنِ وُرِے عَٻُواْيٜىٰ؞ أَبِنْ ڨَمَ نٜىٰ غَ يَهْوٜىٰهْ ؞› «سَيْ دُكَنْ جَمَعَ سُأَمْسَ سُثٜىٰ، ‹أَمِينْ!›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“ ‘La'ananne ne mutumin da ya sassaƙa, ko ya ƙera gumaka, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannun mai sana'a, ya kafa ta a ɓoye.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’