Deuteronomy 4:32 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ku bincika dukan tarihi mana, tun daga lokacin da Allah ya halicci mutane a cikin duniya har yă zuwa yanzu; ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«كُبِنْثِكَ دُكَنْ تَارِيحِ مَنَ، تُنْدَغَ لُواْكَثِنْ دَ اللَّهْ يَحَلِثِّ یَنْ أَدَمْ عَثِكِنْ دُونِيَا حَرْ ذُوَا يَنْذُ؞ كُسَاكٜىٰ تَمْبَيَ دَغَ وَنَّنْ إِيَاكَرْ سَمَ ذُوَا وَنْثَنْ، كُواْ وَنِ أَبُ مَيْغِرْمَ إِرِنْ وَنَّنْ يَتَٻَ ڢَرُوَ؟ كُواْ كُوَ أَنْتَٻَ جِنْ لَابَرِ إِرِنْسَ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ku tambaya mana, ko a kwanakin dā kafin zamaninku, tun ma daga lokacin da Allah ya yi mutum a duniya, ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?