Deuteronomy 5:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta ’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَذَاكَ رُسُنَ مُسُبَ، كُواْ كَيِ مُسُ سُجَّدَبَ، غَمَا نِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكَ، اللَّهْ نٜىٰ مَيْ بُڧَاتَرْ ثِكَكِّيَرْ ڧَوْنَرْكَ، مَيْ حُكُنْتَ یَیَ سَبُواْدَ ذُنُبَنْ إِيَايٜىٰنْسُ حَرْ ذُوَا ڟَارَا تَ عُكُ دَ تَهُطُ تَوَطَنْدَ سُكَڧِينِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Kada ka yi musu sujada, ko ka bauta musu, gama ni Ubangiji Allahnka, Allah mai kishi ne, nakan hukunta 'ya'ya, da jikoki saboda laifin iyaye waɗanda suka ƙi ni.