Deuteronomy 7:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka, ku sani cewa Ubangiji Allahnku, shi ne Allah; shi Allah ne mai aminci, yana kiyaye alkawarinsa na ƙauna ga tsararraki dubu na waɗanda suke ƙaunarsa suke kuma kiyaye umarnansa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ، سَيْ كُسَنِ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ شِينٜىٰ اللَّهْ ، اللَّهْ مَيْ أَمِنْثِ نٜىٰ، مَيْ كِيَايٜىٰ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ، مَيْ نُونَ ڧَوْنَرْسَ مَرَرْ ثَنْجَاوَا غَ یَیَ حَرْ ذُوَا ڟَارَا تَدُبُو نَوَطَنْدَ سُكٜىٰ ڧَوْنَرْسَ، سُنَ كُمَ كِيَايٜىٰ عُمَرْنَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Domin haka sai ku sani Ubangiji Allahnku shi ne Allah, Allah mai aminci, mai cika alkawari, mai nuna ƙauna ga dubban tsararraki waɗanda suke ƙaunarsa, suna kuma kiyaye umarnansa.