Ecclesiastes 5:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kada ka bar bakinka ya kai ga yin zunubi. Kada kuma ka kai ƙara wurin ɗan saƙon haikali cewa, “Alkawarin da na yi kuskure ne.” Me ya sa Allah yake fushi a kan abin da ka faɗa har yă lalatar da aikin hannuwanka?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَدَ كَيَرْدَ بَاكِنْكَ يَكَيْكَ ثِكِنْ ذُنُوبِ، دُواْمِنْ كَدَكَثٜىٰ وَڢِرِسْتِ «نَايِ ضَنْڟُوَا ثِكِنْ كُسْكُرٜىٰنٜىٰ؞» دُوانْمٜىٰ ذَاكَسَا اللَّهْ يَيِ ڢُشِے دَكَيْ، حَرْ يَهَلَّكَ عَيْكِنْ حَنُّوَنْكَ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Kada ka bar maganar bakinka ta kai ka ga yin zunubi, har ka ce wa manzon Allah, ba haka kake nufi ba. Don me za ka sa Allah ya yi fushi da kai, har ya hallakar da abin da ka yi wahalarsa?