Ecclesiastes 6:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Allah yakan ba mutum dukiya, da wadata da kuma girma, don kada yă rasa abin da ransa yake so, amma Allah bai ba shi zarafin more su ba, a maimakon haka ma sai baƙo ne yă more su. Wannan ba shi da amfani, mugun abu ne ƙwarai.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
اللَّهْ يَكَنْ بَا وَنِ مُتُمْ دُوكِيَ دَ أَبِنْ مَلَّكَ دَ غِرْمَ، عِ، حَرْ دَ كُواْوَنٜىٰ أَبِنْدَ يَكٜىٰسُواْ أَ رَايُوَا؞ دُكْدَهَكَ اللَّهْ بَيْ يَرْدَ يَجِ دَاطِنْ وَطَنَّنْ أَبُبُوَبَ؞ أَ مَيْمَكُوانْ حَكَ وَنِ بَڧُواْ نٜىٰ ذَيْجِے دَاطِنْسُ؞ وَنَّنْ مَا بَنْظَنٜىٰ، مُوغُنْ أَبُ نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Allah yakan ba wani mutum dukiya, da daraja, da wadata, i, da kowane abu da yake bukata. Amma bai ba shi iko ya more su ba. A maimakonsa wani baƙo ne zai more su. Wannan aikin banza ne ba kuwa daidai ba ne.