Esther 7:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُنَ ثِكِنْ شَنْ ضُوً إِنَبِے أَ رَانَ تَبِيُ، سَيْ سَرْكِے يَسَاكٜىٰ ثٜىٰ وَ عٜىٰسْتَا «سَرَوْنِيَ عٜىٰسْتَا، مٜىٰكِكٜىٰ بُڧَاتَ؟ ذَاكِ سَامُ؞ مٜىٰنٜىٰنٜىٰ ضُواْڧُوانْكِ؟ كُواْ دَمَا رَبِنْ مُلْكِنَ نٜىٰ، ذَنْبَاكِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A rana ta biyu, sa'ad da suke shan ruwan inabi, sai sarki ya sāke ce wa Esta, “Mece ce bukatarki, sarauniya Esta? Za a yi miki. Mene ne roƙonki? Za a ba ki, ko da rabin mulkina ne.”