Esther 9:12 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sarki ya ce wa Sarauniya Esta, “Yahudawa sun karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar, da kuma ’ya’ya maza goma na Haman a mazaunin masarauta a Shusha. Me suka yi a sauran lardunan sarki? Yanzu kuma mene ne roƙonki? Za a ba ki. Mece ce bukatarki? Za a biya miki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے يَثٜىٰ وَ سَرَوْنِيَ عٜىٰسْتَا «عَثِكِنْ وُرِے مَيْ كَتَنْغَ أَ شُوشَنْ كَطَيْ، يَهُودَاوَا سُنْ كَشٜىٰ سُنْ كُمَ هَلَّكَ مُتَنٜىٰ طَرِے بِيَرْ دَ كُمَ یَیَنْ هَامَٰنَ غُدَا غُواْمَ؞ تُواْ، وَ يَسَنْ أَبِنْدَ سُكَيِ عَثِكِنْ سَوْرَنْ يَنْكُنَنْ مُلْكٍ؟ مٜىٰ كُمَ كِكٜىٰ بُڧَاتَ؟ ذَاكِ سَامُ؞ مٜىٰنٜىٰنٜىٰ ضُواْڧُوانْكِ؟ ذَنْ بَاكِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai sarki ya ce wa sarauniya Esta, “A Shushan, masarauta, Yahudawa sun kashe mutum ɗari biyar da kuma 'ya'yan Haman guda goma. Mene ne suka yi a sauran lardunan sarki? Mece ce kuma bukatarki? Za a yi miki. Mene ne kuma roƙonki? Za a ba ki.”