Exodus 14:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ عَكَ ڢَطَا وَسَرْكِنْ مَصَرْ ثٜىٰوَ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ سُنْ غُدُ، سَيْ ڢِرْعَوْنَ دَ دَتَّاوَنْسَ سُكَ ثَنْجَ تُنَانِنْسُ غَمٜىٰدَ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا سُكَثٜىٰ «كَيْ! مٜىٰ مُكَيِ كٜىٰنَنْ دَ مُكَ بَرْ دُكَنْ وَطَنَّنْ بَايِ سُنْ تَڢِے؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da aka faɗa wa Sarkin Masar jama'a sun gudu, sai shi da fādawansa suka sāke tunaninsu game da jama'ar, suka ce, “Me muka yi ke nan, da muka bar Isra'ilawa su fita daga cikin bautarmu?”