Exodus 15:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ «عِدَنْ ذَاكُ كَسَ كُنّٜىٰ غَ مَغَنَاتَ، نِے دَ نَكٜىٰ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ، كُكُمَيِ أَبِنْدَ يَكٜىٰ دَيْدَيْ أَعِدُواْنَ، كُيِ بِيَيَّ دَ عُمَرْنَيْنَ، كُكِيَايٜىٰ ڧَٰعِدُواْدِنَ، نِے كُمَ بَذَنْ عَيْكَ مُكُ دَ ثُوتُتُّكَنْدَ نَعَيْكَ وَ مَصَرَاوَا بَ؞ غَمَا نِنٜىٰ يَهْوٜىٰهْ مَيْ وَرْكَرْ دَكُو؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya ce, “In za ku himmantu ku yi biyayya da ni, ni da nake Ubangiji Allahnku, sai ku aikata abin da yake daidai a gare ni, ku kuma kiyaye umarnaina da dokokina duka, to, ba zan sa muku cuce-cuce irin waɗanda na sa wa Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”