Exodus 19:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ وَ مُوسَٰى «غَاشِ، نِے ذَنْذُواْ وُرِنْكَ عَثِكِنْ دُهُنْ غِرْغِجٜىٰ، دُواْمِنْ جَمَعَرْ سُجِ يَايِنْ دَ نَكٜىٰ مَغَنَ دَكَيْ، دُواْمِنْ كُمَ دَغَ يَنْذُ سُدِنْغَ أَمِنْثٜىٰوَ دَكَيْ؞» سَعَدَّ مُوسَٰى يَمَيَرْ وَ يَهْوٜىٰهْ دَ أَمْسَرْ دَ جَمَعَرْ سُكَ بَايَرْ،
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ga shi, ni da kaina, ina zuwa a gare ka cikin duhun girgije, domin jama'a su ji sa'ad da nake magana da kai, domin su amince da kai tutur.” Musa kuwa ya mayar wa Ubangiji da amsar da jama'ar suka bayar.