Exodus 20:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta ’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَذَاكَ رُسُنَ مُسُبَ، كُواْ كَيِمُسُ سُجَّدَ، غَمَا نِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكَ، اللَّهْ نٜىٰ مَيْ بُڧَاتَرْ ثِكَكِّيَرْ ڧَوْنَرْكَ، مَيْ حُكُنْتَ یَیَ سَبُواْدَ ذُنُبَنْ إِيَايٜىٰنْسُ حَرْ ذُوَا ڟَارَا تَ عُكُ دَ تَهُطُ تَوَطَنْدَ سُكَڧِينِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Kada ka rusuna musu, kada kuwa ka bauta musu, gama ni Ubangiji Allahnka, mai kishi ne. Nakan hukunta 'ya'ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina.