Exodus 33:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ وَ مُوسَٰى «تَاشِ دَغَ نَنْ، كَيْ دَ جَمَعَرْدَ كَڢِتَرْ دَسُو دَغَ ڧَسَرْ مَصَرْ، كُتَڢِے ڧَسَرْدَ نَرَنْڟٜىٰوَ إِبْرَٰهِيمْ دَ إِسْحَٰڧَ دَ يَعْڧُوبَ ثٜىٰوَ ‹غَ ذُرِيَرْكُ ذَنْبَادَ ڧَسَرْ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi, ka kama hanya, kai da jama'ar da ka fisshe su daga ƙasar Masar, zuwa ƙasar da na rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, na ce, ‘Ga zuriyarka zan ba da ita.’