Exodus 4:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا مُوسَٰى يَثٜىٰ وَ يَهْوٜىٰهْ «يَا يَهْوٜىٰهْ ، نِے بَ مَيْ عِيَ مَغَنَ بَنٜىٰ، بَنْتَٻَ عِيَ مَغَنَ بَ، كُواْ عَيَنْظُ مَا، بَايَنْدَ كَيِ مَغَنَ دَنِے بَاوَنْكَ؞ نِے مَيْ نَوْيِنْ بَاكِ نٜىٰ، هَرْشٜىٰنَ مَا حَكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangijina, ni ba mai lafazi ba ne, ban taɓa zama ba, ko a yanzu ma, bayan da ka yi magana da bawanka, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”